1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

FIFA: Guguwar sauyi na neman tafiya da Infantino

August 5, 2026

Shugaban FIFA Gianni Infantino, ya kira taro da manyan jami'an hukumar a Maroko, sakamakon matsin lamba da ya ke fuskanta tun bayan ayyana shirin sayar da hannun jari.

https://p.dw.com/p/5II2e
Shugaban FIFA Gianni Infantino
Shugaban FIFA Gianni Infantino Hoto: Darryl Dyck/The Canadian Press/AP Photo/dpa/picture alliance

Tun da fari dai, tsohon manajan Arsenal, Arsène Wenger, ya nesanta kansa dangane da wannan dambarwa, inda ya ce ba shi da hannu a shirin kafa kamfanin masu neman zuba jari a hukumar. Shirin ya haɗa da sayar da kashi 20 cikin 100 na kamfanin ga masu saka hannun jari, lamarin da ya fuskanci adawa mai ƙarfi daga UEFA da sauran kungiyoyin kwallon kafa ta duniya.

Karin bayani:FIFA ta yi amai ta lashe kan shirinta na sayar da hannun jari 

A halin yanzu dai, ƙasashen Afirka da Kudancin Amurka da Oceania na ci gaba da mara wa Infantino baya, yayin da ƙasashen Asiya ke nazari wajen tantance makomarsa. Wasu ƙasashe irin su Qatar da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa sun nuna goyon bayansu ga Infantino.